Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Sojojin gwamnatin yahudawa sun sanar da hare-haren makamai masu linzami na Iran zuwa yankunan da aka mamaye 'yan mintuna kaɗan da suka wuce.
Sojojin gwamnatin mamaya sun yi iƙirarin cewa tsarin tsaron gwamnatin yana bibiyar barazanar harin domin fuskantar shi.
Haka kuma wasu majiyoyin Ibrananci sun bayyana cewa a biranen Haifa da Nazareth an ji karar fashe-fashe. Wannan aikin ladabtarwa daga sojojin Iran ya biyo bayan da gwamnatin yahudawa tare da goyon bayan Amurka gaba daya suka yi ta keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka kafa a fagen Lebanon akai-akai.
..............................
Your Comment